Mahangar Musulunci: Fahimtar muhimmancin zuciya mara karaya kan Addu'a

top-news

Daga Ibrahim Musa 

 A fagen imani, lamarin addu'a lamari ne mai zurfi na sirri da tsarki.  Ga Musulmai, addu'a ba aikin al'ada ba ne kawai, amma babbar hanya ce ta munajati da Ubangiji, tattaunawa ta ruhaniya wacce ta ketare iyakokin lokaci da sarari. Ginshikin wannan tafiya ta ruhaniya ita ce manufar kiyaye zuciya marar karaya, ko da a gaban addu'o'in da ba a amsa ba.

 A Musulunci, ana daukar zuciya a matsayin wurin zama na imani, jirgin da mutum yakan hau don gamuwa da Allah (SWT).  Ita ce wurin ikhlasi, tawali'u, da ibada a cikin addu'a.  Muhimmancin zuciya mara karaya a cikin addu'a yana nuni ne da imani da buwaya da hikimar Allah.  Yayin da muminai na iya yin addu'a da roƙon sa bisa buƙatu da sha'awarsu, sun yi amanna da cewa tsare-tsaren Allah sun fi gaban fahimtar mutum.

 Alƙur'ani mai girma, littafin Musulunci tilo da babu kuskure a cikin sa, ya sha nanata muhimmancin haƙuri da kuma dogaro da hukuncin Allah.  Suratul Baqarah (2:153) tana cewa, “Ya ku waɗanda suka yi imani, ku nemi taimako da haƙuri da addu’a, lallai Allah yana tare da masu haƙuri”.  Wannan ayar tana kunshe da mahangar Musulunci game da addu'a - ba wai kawai neman taimakon Ubangiji ba ne, har ma da yin haƙuri da juriya.
A cikin aƙidar Musulunci, manufar "Rida bil Qada" ko gamsuwa da hukuncin Ubangiji yana da muhimmanci.  Yana tattare da yarda da yardar Allah da falala da tawali'u, ko da kuwa bukatun ka sun rabu da son zuciya.  Imam Ali ibn Abi Talib, ƙani kuma surukin Annabi Muhammad (saw) cikin balaga ya bayyana wannan ra’ayin, yana mai cewa: “Ka sani cewa abin da ya shige ka (kuma ka kasa samu) bai kasance ba zai same ka, kuma abin da ya same ka, dama ba zai wuce ka ba."

Wannan fahimta mai zurfi tana jaddada imani da cewa addu'o'in da ba a amsa ba, ba alamar Allah ya yi watsi da kai ba ne ko rashin kulawa daga Allah.  A'a, shaida ce ta hikimar Allah da kuma falalarsa mara iyaka.  Kamar yadda iyaye masu ƙauna za su iya riƙe wasu buƙatu daga ɗansu don amfanin hakan ga dan nasu na dogon lokaci, Allah cikin hikimarSa marar iyaka, yana iya jinkirta ko hana wasu addu'o'in don bai wa muminai abin da ke da fa'ida da gaske ga haɓakar ruhaniyarsu da walwalarsu a gaba.

Bugu da ƙari, hadisan Musulunci suna jaddada kafin ikon canza mutum da musiba da gwaji suke da shi. Imam Ali, wanda ake girmama shi a matsayin abin koyi na hikima da takawa a Musulunci, ya taba cewa, "Zaƙin haƙuri yana cikin dacin sakamakonsa."  Masifu, gami da addu’o’in da ba a amsa ba, suna zama a matsayin wata tukunyar karfe ta inda muminai ke tsarkake halayensu, da ƙarfafa imaninsu, da zurfafa tawakkali ga Allah.

A yayin addu’o’in da ba a amsa ba, ana kwadaitar da musulmi da su koma ga ayyukan ibada da kankan da kai a matsayin hanyar neman kusanci zuwa ga Allah.  Karatun ayoyin Alqur'ani, da shagaltuwa da sallolin Nawafil, da ayyukan sadaka, duk wadannan hanyoyi ne da muminai ke bi don samun natsuwa da abinci na ruhi.

Bayan haka, hadisai na Musulunci sun ba da muhimmanci sosai kan ceton Ahlul Baiti (iyalan Annabi Muhammad) a matsayin masu shiga tsakani, tsakanin bil'adama da Ubangiji.  Musulmai sun yi imani da cewa Imamai, musamman Imam Ali da Imam Mahdi (Mai ceton da ake jira), suna da matsayi na musamman a wurin Allah kuma suna iya yin ceto a madadin muminai.

 A ƙarshe, a mahangar Musulunci, ba za a iya kure muhimmancin kiyaye zuciya kada ta karaya a kan addu'a ba.  Duk da cewa sanin addu'o'in da ba a amsa ba na iya gwada imani da haƙurin mai yin addu'r, amma a ƙarshe yana tunatar da mutum  ikon Allah da hikimar Allah (SWT).  Ta hanyar haɓaka haƙuri, amana, da gamsuwa da ƙaddarar Ubangiji, muminai za su iya tafiyar da rikitattun ƙalubalen rayuwa tare da juriya da falala, da sanin cewa tsare-tsaren Allah a kodayaushe don amfaninsu ne.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *